Friday 11 July 2014

DAN KARAMIN MUGU

Wani yaro ne babansa ya tafi da shi masallaci ranar Juma'a, suna cikin tafiya sai suka gamu da wani wada, shi ma zai shiga masallacin, sai yaron ya ce ma wadan, "Kai ma babanka ne ya zo da kai?"

Ashe wadan nan haushi ya kama shi, kuma sai aka yi katari sun yi shimfida a wuri daya. Da zarar an yi sujada, sai wada ya zabga wa yaron nan mintsini, yaro ya yi ta kara, aka rasa abin da ke faruwa.

Tun daga ranar nan, duk inda yaron ya ga wada, sai ya ce, "Lah! ga dan karamin mugun nan!" hahahaha...

Shin wai dan karamin mugun nan bafulatani ne ko kanuri?

No comments:

Post a Comment