Friday 11 July 2014

BANZA TA KORI WOFI

Wani saurayi ne da gidansu ke kusa da makabarta, kullum idan ya hawo mota ko babur baya biya, ana zuwa daidai makabartar nan sai ya ce a sauke shi, ana sauke shi sai ya nuna ai shima mataccene, fatalwa ya yi ya fito yawon shakatawa, kawai sai ya shige makabartar.

Ana cikin haka ne wata rana ya hawo babur din wani dan achaba me shegen naci, bayan sun zo daidai makabartar sai saurayin nan yace, "Tsaya na sauka anan" yana sauka sai yai kokarin shiga makabarta kamar yadda ya saba, amma sai Dan achaba ya rike shi ya ce ya ba shi kudinsa, to anan ne saurayin nan ya ce da shi shi fa fatalw ne ba me rai bane kuma gida ya kawoshi (wato makabarta).

Nan take Dan achaba ya ce to su shiga ya ba shi kudinsa. Haka kuwa aka yi, suna shiga abokin namu ya je kan wani kabari yace, "Danlami bani naira tamanin (#80) na ba wa wannan Dan achaban kudinsa", ai kafin ya gama rufe baki kawai sai suka ga wani hannu ya bullo da naira dari (#100) yace, "Karbi wannan ka ba shi, ya ba mu chanji, ni ma ragowar kudina ke nan."

Ai da Saurayin nan da Dan achaba sai kowa ya cika rigarsa da iska yayi takansa. Ashe wani Mahaukaci ne yazo ya kwanta a ciki, banza ta kori wofi ke nan.

A ganinku, tsakanin saurayin da Dan achaba wa zai fi wani gudu?

No comments:

Post a Comment