Friday 11 July 2014

ALLAH YA SA KU MUTU

Wata rana, da yamma, wani mahaukaci ya zo zai wuce ta gaban majalisar wasu samari, sai ya dube su ya ce, Allah ya sa duk ku mutu! Sai kow ya kyale shi. Sai ya kara cewa, Allah ya sa duk ku mutu! Suka kara yin banza da shi. Da mahaukacin ya ga babu wanda ya tanka masa, sai ya wuce ya na ta dariya.

Bayan ya wuce sai samarin nan suka ci gaba da hirarsu, su na cewa, mahaukacin banza, in ban da mahaukaci wa ke so ya mutu?

Ran nan kuma sai mahaukacin nan ya kara dawowa wurin samarin nan zai wuce, sai ya dube su ya ce, Allah ya sa duk ku shiga Aljanna. Sai duk suka amsa da sauri, Amin, Amin, Allah ya sa. Mahaukaci ya dube su ya fashe da dariya ya ce mahaukatan banza! Kun taba ganin an shiga Aljanna ba a mutu ba? Ya wuce ya na ta dariya, ya barsu nan cikin tunani.

To wai me ya sa muke tsoron mutuwa ne? Hala bamu shirya mata ba? To me ya ke hana mu shirya ma zuwanta? Don haka kowa ya yi wa kansa wa'azi!

Allah ya bamu ikon karba kira cikin shiri.

No comments:

Post a Comment