Friday 11 July 2014

KAMSHIN ALJANNA

A kasuwar duwatsu masu daraja akwai wani tsoho mai gyaran karyayyun zobuna da sarkoki da sauran abubuwan da aka yi da duwatsu masu daraja kuma yana sayarwa.

Wata rana yana cikin shagonsa, sai wani mutum mai ban mamaki ya shigo ya kawo masa gyaran zobensa. Abin mamakinsa kuwa shi ne duk gashin da ke jikinsa fari ne tas, sannan kuma tufafin jikinsa su ma farare ne, haka hularsa, kai har takalmin mutumin nan farare ne tas, sai daukar ido su ke yi, ga kamshi sai tashi ya ke yi daga jikin mutumin.

Mai sahago ya ba shi wuri ya zauna, shi kuma ya soma gyara ke nan sai ga wasu mutane biyu, mata da miji, sun shigo suka dudduba sai suka ce ya taso ya ba su kaya. Sai ya ce, "Don Allah ku jira na sallami wannan bawan Allan." Ya nuna musu mutumin nan.

Ga mamakinsa sai ya ga sun canza masa kallo, suka dudduba ko'ina, suka yi kamar ba su ga bakon mutumin nan ba. Mai shago ya ga suna magana kasa-kasa, amma bai iya jin me suke cewa. Daga karshe sai suka yi waje da sauri, shi kuma ya ci gaba da aikinsa.

Can kuma sai ga wani mutumin ya shigo shagon a uzurce, ya ce, "Dattijo don Allah sauri na ke yi, dan gyara mini sarkar nan yanzu." Sai mai shago ya ce, "To dan jira ni kadan na karasa wa wannan bawan Allan aikinsa." Sai ya ga mutumin sai waige-waige ya ke yi, ya ce, "Haba dattijo, ni dai ban ga kowa ba, ko dai tsufa ne ya fara taba ka?" Sai ya yi waje abinsa.

Da mutumin nan mai fararen kaya ya ga haka, sai ya ce, "Malam ni fa ba kowa ne ke iya ganina ba, don ni ba mutum ba ne, ni mala'ika ne, na zo ne na yi maka albishir saboda irin yadda kake gudanar da harkokinka tsakani da Allah, shi ya sa Allah ya tanadar maka Aljanna ta musamman. Yanzu haka daga cikinta na fito ka ga wannan ma daga can na zo da shi." Sai ya fito da wani kyalle mai kyau, mai shago bai taba ganin kyalle mai kyawunsa ba ya ce masa, "Sunsuna ka ji yadda kamshin Aljannarka ya ke."

Da tsoho ya ji labarin Aljannah, ai cikin gaggawa ya amshi kyalle ya kai hanci ya shasshaka shi da karfi. HABA AI SAI FARKAWA YA YI YA GAN SHI A ASIBITI.

Ashe mutanen nan duk 'yan 419 ne suka yiwo shiri don su cuce shi. Allah ka tsare mu da sharrin 'yan damfara, Amin.

No comments:

Post a Comment